in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya ta sake nanata matsayinta game da batun tekun kudancin Sin
2016-06-01 13:39:34 cri
Mataimakin firaministan kasar Libya da ke ziyara a kasar Tunisiya Moussa Al-koni ya sake nanatawa a jiya Talata cewa, Libya ta nuna goyon baya da tsayawa haikan game da batun tekun kudancin kasar Sin kamar yadda ya ke kunshe cikin sanarwar Doha, wadda kasashen Larabawa suka cimma ra'ayi guda a kai.

Al-Koni ya bayyana a yayin da ya ke ganawa da jakadan Sin da ke kasar Libya Li Zhiguo a wannan rana cewa, Libya ta sake nanata cewa, za ta nuna goyon baya tare da tsayawa haikan game da batun tekun kudancin kasar Sin kamar yadda ya ke kunshe cikin sanarwar Doha, wadda aka fitar a yayin taron ministocin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da kasashen Larabawa karo na 7 da da aka yi a ranar 12 ga watan Mayu. Libya tana ganin cewa, ya kamata a bi ka'idar warware matsalolin yankunan kasa da ruwa ta hanyar shawarwari. Libya tana goyon bayan kasashen da batun tekun kudancin kasar Sin ya shafa da su martaba yarjejeniya, da daidaito da aka cimma tsakanin kasashen da ke wannan yanki, don yin shawarwari cikin aminci, ta hakan ne za a warware wadannan riginginmu cikin ruwan sanyi.

Haka kuma Al-Koni ya ce, an shiya taron ministoci karo na 7 na dandalin tattaunwar hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa cikin nasara, lamarin da ya tsara alkiblar raya hadin gwiwar sada zumunta a sabon yanayin da muke ciki.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China