in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta dauki matakai da dama don tabbatar da tsaro a yayin taron kolin G20 a birnin Hangzhou
2016-08-30 13:55:05 cri
Bisa halin yaki da ta'addanci na kasa da kasa da kalubalen duniya da ake fama da shi, Sin ta dauki matakai da dama, don tabbatar da tsaro a yayin gudanar da taron kolin kungiyar G20 karo na 11, da zai gudana a ranekun 4 zuwa 5 ga watan Satumba a birnin Hangzhou.

Wannan ne karo na farko da kasar Sin za ta karbi bakuncin gudanar da taron kolin na G20, kana shi ne batun diplomasiyya mafi muhimmanci ga kasar ta Sin a bana. Hakan ne kuma ya sa aka dauki matakan tabbatar da tsaro a matsayin koli, a yayin taron kolin na G20.

Ga misali, za a yi amfani da fasahar gano asalin mutane ta hanyar duba fuska, domin kara tabbatar da tsaro a muhimman yankuna. Kana hukumomin da abun ya shafa, za su inganta tsarin rajistar sunaye na gaskiya, wanda za a yi amfani da shi a Otel Otel, da a wuraren sufuri, da hidimar samar da yanar gizo da dai sauransu.

Kaza lika domin kandagarkin faruwar al'amura na ba tsammani, an kafa wani rukuni na sintiri a birnin Hangzhou, inda tuni 'yan sandan birnin suka yi gwajin aikin tashoshin bincike a hanyoyin motoci guda 172, don tabbatar da tsaro a dukkan hanyoyin motoci dake birnin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China