in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masana: Za a gabatar da dabarar kasar Sin kan daidaita tattalin arzikin duniya a taron G20
2016-08-29 12:11:58 cri
Za a gudanar da taron koli karo na 11 na shugabannin kungiyar kasashe 20 masu karfin tattalin arziki (G20) a birnin Hangzhou dake gabashin kasar Sin, daga ranar 4 zuwa 5 ga watan Satumba. Kasancewar kasar Sin ce za ta karbi bakuncin taron, ya sa bangarori daban daban na duniya suna jiran ganin kasar za ta gabatar da sabuwar dabara ta kokarin daidaita tsarin tattalin arzikin duniya. Haka kuma a ganin wasu masanan kasar Sin, shawarar da kasar Sin za ta gabatar a wajen taron za ta taimakawa kokarin raya tattalin arzikin duniya.

Chen Fengying, wata manazarciyar huldar kasa da kasa tana ganin cewa, kasar Sin a yanzu haka tana mai da hankali kan kirkiro sabbin fasahohi don samun ci gaban tattalin arziki. Hakan a cewarta na nufin yadda za a yi amfani da wasu damammakin da suka shafi cigaban wasu fasahohin masana'antu, da tattalin arzikin da ake kokarin raya shi bisa tushen alkaluma, don kirkiro sabbin fasahohi, ta yadda za a samar da wani sabon tsarin da zai sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya.

A nasa bangare, Zhao Xijun, masani a fannin hada-hadar kudi na jami'ar jama'a ta kasar Sin ya ce, yanzu kasar Sin ta dora muhimmanci sosai ga manufar gyara tsarin tattalin arziki a kasar, wadda ta kasance daya daga cikin muhimman manufofin kasar, ban da manufofin kudi da na harkar hada-hadar kudi. Don haka yana sa ran ganin kasar Sin ta gabatar da shawarar gyara tsarin tattalin arziki a wajen taron na G20 don neman kyautata yanayin tattalin arzikin duniya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China