in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen kasashen Afirka sun yi kira da a warware batun tekun kudancin kasar Sin ta hanyar yin shawarwari
2016-07-15 15:50:55 cri
Game da hukuncin da aka yanke kan batun tekun kudancin kasar Sin, ministocin harkokin wajen kasashen Afirka dake halartar taron koli na kungiyar AU a kasar Ruwanda sun bayyanawa 'yan jarida cewa, kamata ya yi bangarorin da abin ya shafa su yi shawarwari kai tsaye don warware wannan takadama.

Ministan harkokin wajen kasar Liberiya Marjon Kamara ya bayyana cewa, gwamnatin kasarsa ta nuna goyon baya kan matsayin da Sin ta dauka kan wannan batun, a ganinta, ya kamata a warware batun ta hanyar yin shawarwari bisa dokokin kasa da kasa da abin ya shafa.

A nasa bangare, ministan harkokin wajen kasar Senegal Mankeur Ndiaye ya bayyana cewa, kafin wannan hukunci, Sin da Philippines sun taba cimma daidaito kan warware batun tekun kudancin Sin ta hanyar yin shawarwari, dangane da haka, kasar Senegal ta yi kira ga kasashen da abin ya shafa da su bi daidaiton da aka cimma, da warware batun ta hanyar yin shawarwari, da tabbatar da zaman lafiya da tsaro a tekun.

Ban da wannan kuma, mataimakin shugaban kwamitin kungiyar AU Erastus Mwencha ya bayyanawa 'yan jarida cewa, bisa ra'ayin AU, hanya mafi kyau wajen warware batun tekun kudancin Sin ita ce yin shawarwari na kai tsaye tsakanin bangarorin da abin ya shafa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China