in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana fatan kasar Australia zata yi takatsantsan kan batun tekun kudancin kasar Sin
2016-07-15 11:10:44 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a jiya Alhamis 14 ga wata cewa, Australia ba kasar da batun tekun kudancin kasar Sin ya shafa ba ce. Sin tana fatan kasar Australia za ta cika alkawarin kaucewa tsoma baki kan batun ikon mallaka da kuma bai shafar ta ba, da yin takatsantsan, da nisantar yi aikin da zai kawo illa ga zaman lafiya a yankin da bunkasuwar dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin.

A kwanakin baya, babbar jami'ar kasar Australia ta yi furuci game da hukuncin da aka yanke kan batun tekun kudancin kasar Sin cewa, hukuncin yana da karfi, ya kamata bangarori daban daban su bi hukuncin, kana kasar Australia tana da ikon ratsa da keta sararin sama bisa tanadin dokokin kasa da kasa.

Game da wannan batu, Lu Kang ya bayyana cewa, Sin ta riga ta tuntubi kasar Australia, domin bayyana mata rashin amincewarta.

Lu Kang ya kara da cewa, hukuncin da aka yanke ba zai yi tasiri ga ikon mallakar tekun kudancin kasar Sin da moriyar tekun, kuma kasar Sin ta nuna rashin amincewarta ga duk wani irin aikin da za a gudanar bisa hukuncin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China