in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan majalisar dokokin Turai: Ya kamata a warware batun tekun kudancin Sin ta hanyar yin shawarwari da diplomasiyya
2016-07-15 11:00:33 cri
Dan majalisar dokokin Turai Helmut Scholz ya bayyana a jiya Alhamis 14 ga wata cewa, ya kamata a warware rikicin dake tsakanin Sin da kasashen dake makwabtaka da ita a kan teku ta hanyar diplomasiyya, amma ba ta hanyar kotu ba.

Scholz memba na kungiyar GUE / NGL ta majalisar dokokin Turai da ya zo daga kasar Jamus. A wannan rana, ya bayyana a cikin wani sakon E-mail da ya turawa manema labaru, ya nuna cewa, hukuncin da kotun yanke hukunci ta Hague ta yanke ba zai maye gurbin shawarwarin da kasa da kasa suka yi don warware batun tekun kudancin kasar Sin ba. Ya ce, tilas ne kasashen da abin ya shafa su fara yin shawarwari cikin hanzari, wadanda ya kamata su maida hankali ga fannoni uku wato magance yin yaki, tabbatar da tsaron zirga-zirga, da kuma yin hadin gwiwar moriyar juna.

Scholz ya jaddada cewa, ana bukatar bangarori daban daban da abin ya shafa su girmama da amincewa da juna, wanda zai taimakawa wajen warware wannan matsala. Sin ta riga ta bayyana ra'ayinta na fatan yin shawarwari, ya kamata kasashen dake yankin su bi sahun kasar Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China