in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jaddada kokarin tabbatar da lafiyar jama'a
2016-08-21 12:36:36 cri
A ranakun 19 da 20 ga wannan wata, an shirya babban taro game da harkokin kiwon lafiya da tsabta a nan Beijing na kasar Sin.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron, kuma ya yi jawabi, inda ya jaddada cewa, dole ne a sanya aikin kiwon lafiyar jama'a a matsayin muhimman al'amari da za a kara mai da hankali wajen bunkasa shi cikin dogon lokaci, ta yadda za a iya tabbatar da ganin an kiyaye lafiyar jama'ar kasar Sin daga dukkan fannoni, a kowane lokaci a yi kokarin gina wani kakkarfan tushe don cimma burin kasar Sin na sake farfadowar al'ummarta a lokacin da ake murnar cika shekaru 100 da kafuwar jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin a shekarar 2021, da taya murnar cika shekaru 100 da kafuwar Jamhuriyar Jama'ar Sin a shekarar 2049.

Bugu da kari Xi Jinping ya jaddada cewa, a cikin dogon lokacin da ya gabata, kasar Sin ta samu ci gaba sosai wajen nune-nunen wata babbar kasa wadda take kokarin sauke nauyin da ya wajaba a kanta na kasa da kasa na kokarin ba da jinya a duk fadin duniya, sakamakon haka, ta samu yabo sosai daga gamayyar kasa da kasa.

Shugaba Xi, ya nemi a kyautata ayyukan kula da lafiya ta gaggawa domin tinkarar al'amuran kiwon lafiya na ibtila'i da ka iya faruwa a sauran kasashen duniya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China