in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 247 sun mutu a sakamakon girgizar kasa da ta auku a tsakiyar kasar Italiya
2016-08-25 13:47:49 cri

A jiya Alhamis da karfe 3 da mini 36 na safe, an yi girgizar kasa mai karfin maki 6 bisa ma'aunin Richter a tsakiyar kasar Italiya, wadda ta shafi birane da garuruwa fiye da goma dake iyakar tsakanin yankin Lazio da na Marche. Ya zuwa yanzu, mutane a kalla 247 sun mutu a sakamakon girgizar kasar, kana garin Amatrice dake arewa maso yammacin yankin Lazio ya fi ko ina fama da bala'in.

Koda yake yanzu ana gudanar da aikin neman mutane da sauran ayyukan ceto, sai dai kasancewar girgizar kasar ta auku ne da daddare, gine gine sun danne mutane da yawa a gidajen su yayin da suke yin barci, kana babu hanyoyin motoci masu kyau a garin Amatrice dake yankin Appennino. Ana dai hasashen cewa, yawan mutanen da suka mutu ko raunata a sakamakon girgizar kasar zai karu.

A safiyar ranar Laraba ne masu bada ceto daga yankuna da kewaye suka isa wurin, kana yanzu sojoji da 'yan sanda sun shiga ayyukan ceton, kuma masu aikin sa kai daga wurare daban daban sun isa wurin don bada taimako. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China