in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutuwar mutane ya karu zuwa 413 sakamakon girgizar kasa a Ecuador
2016-04-19 10:48:28 cri
A jiya Litinin, ministan kyautata tsaro na kasar Ecuador ya sanar da cewa, yawan mutanen da suka rasu ya karu zuwa 413 sakamakon abkuwar bala'in girgizar kasa mai karfin digiri 7.8 bisa ma'aunin Richter a ranar 16 ga wata a yankunan kusa da teku dake arewa maso yammacin kasar.

A jiya, shugaban kasar Rafael Correa Delgado ya yi rangadi a yankuna masu kusa da teku da bala'in ya fi shafa ta cikin jirgin sama mai saukar ungulu, inda ya furta cewa, girgizar kasar ta haifar na barna mai tsanani, yayin da wasu mutane da yawa suke karkashin buraguzan gine gine. Shi ya sa mai yiwuwa ne yawan mutuwar mutane zai ci gaba da karuwa.

A garin Pedernales dake tsakiyar yankin da girgizar kasar ta faru, an tsugunar da masu fama da bala'in sama da dari daya a rumfunan da aka kafa a wani filin wasan kwallon kafa.

Ma'aikatar harkokin wajen Ecuador ta bayyana cewa, kasashen Bolivia, Switzerland, Spain da sauransu sun tura masu aikin ceto zuwa kasar bi da bi, yayin da aka kebe kayayyakin agajin jin kai zuwa kasar a kai a kai.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China