Sakataren janar na MDD Ban Ki-moon ya ce, ya yi matukar kaduwa bisa labarin afkuwar girgizar kasa mai tsananin gaske wadda ta haddasa hasarar rayuka a kasashen Italiya da Myama da safiyar ranar Larabar da ta gabata, kana ya mika sakon ta'aziyya ga al'ummomi da gwamnatocin kasashen.
Mai magana da yawun MDD Stephane Dujarric, ya shedawa 'yan jaridu cewa, ofishin kula da al'amurran jin kai na MDD yana ci gaba da tuntubar hukumomin kasashen biyu domin bibiyar halin da ake ciki a kasashen biyu.(Ahmad Fagam)