in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jiragen saman sojan Faransa sun kai hari kan IS a Syria
2016-08-23 10:53:44 cri
Ma'aikatar tsaron kasar Farsansa, ta bayar da sanarwa a jiya Lahadi cewa, jiragen saman sojan kasar sun jefa boma bomai, kan na'urorin aikin soja na kungiyar IS dake kasar Syria, harin da ya lalata wata ma'adanar makamai ta kungiyar dake birnin Rekka.

Ma'aikatar tsaron ta bayyana cewa, mako guda kafin hakan, kasar Faransa ta kai farmaki sau da dama ta sama, kan na'urorin kungiyar ta IS dake dab da birnin Mosul na kasar Iraki.

A ranar 13 ga watan Nuwambar shekarar bara ne dai aka kaddamar da farmakin ta'addanci a birnin Paris, fadar mulkin kasar Faransa, hare haren da suka haddasa rasuwar mutane a kalla 130, yayin da mutane kimanin 350 suka ji rauni.

Kungiyar IS dai ta sanar da daukar alhakin kai farmakin, matakin da ya sanya sojojin kasar Faransa karfafa matakan soja da take dauka a kan kungiyar ta IS dake kasashen Iraki da Syria. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China