in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
CIA ta yi gargadin karin hare-haren da mai yiyuwa ne IS za ta kai wa kasashen yammacin duniya
2016-06-17 09:48:51 cri
Kungiyar IS dake kasashen Sham da Iraki tana da shirin kai karin hare-hare kan kasashen yammacin duniya. Mr. John Brennan, direktan babbar hukumar leken asiri ta kasar Amurka CIA ya gaya wa 'yan majalisar dokokin kasar Amurka a ranar Alhamis, sannan ya tabbatar da cewa, mutumin da ake kira shi "lone wolf" da ya kai hari a wani wurin shakatawa a Orlando ba shi da wata dangantaka kai tsaye da kungiyar IS mai tsattsauran ra'ayi.

Brennan ya gaya wa kwamitin kula da aikin leken asiri na majalisar dattawa ta kasar Amurka, cewar kungiyar IS tana da dimbin mabiya masu dauke da makamai wadanda za su iya daukar matakan kai hare-hare a kasashen yammacin duniya. Ya yi gargadin cewa, mai yiyuwa membobin kungiyar IS za su shiga kasashen yammacin duniya a matsayin 'yan gudun hijira.

Bisa alkaluman da Mr. Brennan ya bayar, an ce, ko da yake kungiyar IS, ta rasa yankuna da yawa a kasashen Sham da Iraki, amma har yanzu tana da dakaru masu dauke da makamai wajen dubu 18 zuwa dubu 22, kuma reshenta dake kasar Libya na da dimbin makaman zamani masu hadari sosai.

Direktan hukumar CIA ya kimanta cewa, akwai masu dauke da makamai na kungiyar IS wajen dubu 5 zuwa dubu 8 dake zaune a kasar Libya wadda take kusa da kasashen Turai sosai. Sannan akwai wasu dubu 7 da suke kasar Najeriya, da daruruwa suna kasar Masar da Afghanistan da Pakistan. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China