in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya yi kira ga kafofin watsa labarai da su yayata shirin nan na Ziri daya da hanya daya
2016-07-26 20:11:59 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi kira ga kafofin watsa labarai da ke kasashen daban-daban na duniya da su taka muhimmiyar rawa wajen yayata shirin nan na Ziri daya da hanya daya.

Shugaba Xi ya yi wannan kiran ne cikin wani sakon taya murna da ya aikawa dandalin hadin gwiwar kafofin watsa labarai game da shirin Ziri daya da hanya daya na wannan shekara da aka bude yau Talata a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

A cikin sakon, shugaba Xi ya yi kira da a hada karfi da karfe wajen gina hanyar siliki maras gurbata muhalli cikin lumana wadda za ta amfana al'ummomin da shirin ziri daya da hanya ya ratsa ta cikinsu.

Taron wanda jaridar people daily ta kasar Sin ta shirya, ya samu halartar wakilan kafofin watsa labarai 212 daga kasashe 101.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China