in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yankin Sahel na fuskantar matsalolin tsaro da na muhalli, in ji Firaministan kasar Senegal
2016-06-14 19:05:12 cri
Firaministan kasar Senegal Mohamed Dionne ya bayyana cewa, babban kalubalen da kasashen da ke yankin Sahel suke fuskanta, shi ne tsaro, baya ga kalubaloli na matsalar canjin yanayi da kuma muhalli.

Firaministan ya bayyana hakan ne lokacin da ya ke jawabi a bikin bude taron ministoci ne na kasashen sashen gabashi da yammacin Afirka game da yaki da hamada karo na 5 da ya gudana a Dakar na kasar Senegal.

A cewarsa, matsalar tsaron tana haifar da karuwar ayyukan ta'addanci, lamarin da ke shafar galibin kasashen da ke yankin na Sahel.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China