Kungiyoyin dai sun amince su dakatar da yajin aikin ne,bayan da shugabanin addinai a kasar suka shiga tsakani.
Tun a cikin watanni hudun da suka gabata ne, aka fara samun takun-saka a bangaren Ilimin kasar sakamakon gazawar gwamnati na cika alkawarin da ta yiwa malaman na biyansu albashi da kudadensu na alawus-alawus.(Ibrahim)