in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin dake Jamhuriyar Nijer ya gana da shugaban Nijer
2016-08-14 13:38:39 cri
Jakadan Sin dake Jamhuriyar Nijer Shi Hu, ya gana da shugaban kasar Nijer Mahamadou Issoufou.

Shugaba Issoufou ya bayyana cewa, ya halarci bikin kammala gina asibiti dake da gadaje 500 bisa taimakon kasar Sin ta bai wa Nijer a ranar 2 ga wannan wata, kana ya ziyarci babban ginin asibitin mai dauke da na'urorin aikin kiwon lafiya na zamani, ya nuna gamsuwa ga aikin, sannan ya nuna godiya ga gwamnatin kasar Sin da jama'arta.

A nasa bangare, jakada Shi, ya bayyana cewa, wannan asibiti ya kasance asibiti mafi girma da kasar Sin ta taimakawa kasashen waje wajen ginawa, wanda ya sheda matukar muhimmancin da gwamnatin Sin ke dora ga dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu. Sin tana son yin kokari tare da Jamhuriyar Nijer wajen gudanar da ayyukan asibitin da bada jinya ga jama'ar kasar Nijer yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China