in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 14 sun mutu sakamakon ambaliyar ruwa mai tsanani a kasar Nijer
2016-08-12 11:36:51 cri
Gwamnatin kasar Nijer ta bayar da sanarwa a jiya ranar 11 ga wata cewa, a sakamakon ruwan sama masu tsanani da aka samu a makwannin da suka gabata, sun janyo ambaliyar ruwa a wurare daban daban na kasar, ya zuwa yanzu mutane 14 sun mutu a sakamakon bala'in, yayin da mutane 5 suka ji rauni, yayin da mutane kimanin dubu 40 suke fama da bala'in.

Sanarwar ta nuna cewa, an fi fama da bala'in a birnin Niamey da jihar Tillabery, inda ambaliyar ruwan ta lalata gonaki da hanyoyin motoci da gadoji da dama.

Sanarwar ta kara da cewa, lamarin zai iya janyo karancin hatsi a kasar Nijer sakamakon bala'in da aka samu a manyan yankunan kasar. Don tinkarar matsalar, gwamnatin kasar ta samar da abinci ton 326 don taimakawa jama'a masu fama da bala'in, kuma tana shirin samar da kudi da fasahohi ga yankunan da bala'in ya shafa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China