in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta horas da mayakan Boko Haram 800 da suka tuba a yankin arewa masu gabashin Najeriya
2016-08-02 10:31:19 cri
Gwamnatin Najeriya ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka wajaba don fara horas da mayakan Boko Haram kimanin 800 da suka tduba daga aikata wannan danyen aiki a jihar Gombe da ke yankin arewa maso gabashin kasar.

Jami'in kula da shirin sake tsugunar da mayakan Boko Haram da suka tuba, birgediya janar Bamidele Shaffa ne ya bayyana hakan ga taron manema labarai a garin Gombe. Yana mai cewa, nan ba da dadewa ba, 'yan Boko Haram din da suka tuba za su iso garin Gombe domin fara cin gajiyar wannan shiri, wanda zai fara aiki a sansanin sake tsugunar da tsoffin mayakan.

Ya ce, a lokacin da tsoffin mayakan na Boko Haram suke sansanin samun horon,za a koyar musu illar tsattsauran ra'ayi, matakin da zai taimaka musu sake komawa cikin al'ummominsu ba tare da wata matsala ba.

Shafa ya kuma bayyana cewa, kimanin hukumomin gwamnatin tarayyar Najeriya 14 ciki har da jami'an tsaro ne za su yi aiki a wannan sansani

A na saran horas da tsoffin mayakan na Boko Haram sana'o'I i a kalla 12 (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China