A yayin bikin tunawa da cika shekaru 56 da samun 'yancin kan kasar Cote d'Ivoire, an gudanar da faretin sojoji da kuma ba da lambar yabo a fadar shugaban kasar a jiya Lahadi. Shugaban kasar Alassane Ouattara ya halarci bikin, haka ma rundunonin sojoji 38 sun yi jerin gwano a lokacin gudanar da bikin.(Laouali Souleymane)