Cote d'Ivoire: An kama mutane da dama bayan zanga zangar da ta biyo da wawashe dukiyoyin jama'a
A kasar Cote d'Ivoire, Mutane da dama ne aka kama kuma doka zata yi aikinta bayan wasu karukan gangami da suka janyo mutuwar mutane biyu da kuma lalata gine ginen gwamnati dana masu zaman kansu da dama a Bouake dake tsakiyar kasar mai tazarar kilomita 320 daga birnin Abidjan, in ji gwamnatin kasar, tare da yin alkawarin hukunta dukkan wadanda suke da laifi kan abubuwan da suka faru. Mutane biyu ne aka harbe kana wasu da dama suka jikkata a lokacin artabu tare da jami'an tsaro, a lokacin wadannan zanga zanga. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku