An gurfanar da Simone Gbagbo, uwar gidan tsohon shugaban kasar Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo gaban kuliya.
Uwar gida Simone dai za ta fuskanci hukunci ne a ranar 31 ga watan jiya a wata kotu wadda ta fara sauraron karar da aka shigar gabanta a birnin Abidjan, fadar mulkin kasar ta Cote d'Ivoire.
An dai zargi Simone da laifin cin zarafin dan Adam, da fursunoni, da kuma fararen hula, a yayin rikicin siyasar da ya faru bayan babban zaben kasar da ya gabata. (Lami)