in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso: Faraminista ya yi alkawarin kafa guraben aikin yi fiye da dubu hamsin nan da shekaru biyar
2016-08-06 12:51:06 cri
Faraministan kasar Burkina Faso, Paul Kaba Thieba ya bayyana cewa shirin kasa na ci gaban tattalin arziki da jama'a (PNDES) na mai da hankali wajen kafa guraben aiki yi fiye da dubu 50 a tsawon shekaru biyar masu zuwa wato shekarar 2016 zuwa shekarar 2020.

Da yake magana a ranar Alhamis a yayin wani taron manema labarai, mista Thieba ya nuna cewa adadin wannan kudi na PNDES ya tashi zuwa fiye da Sefa biliyan 15,395, wanda ya tashi fiye da Sefa biliyan 3,079.1 a kowace shekara.

Bisa tanade tanaden da suka shafi wadannan kudade, gwamnatin Burkina Faso na ba da muhimmanci ga albarkatun cikin gida da aka kiyasta zuwa kashi 63,8 cikin 100, kimanin Sefa biliyan 9,825.2, in ji Thieba.

Faraministan ya jaddada cewa burin wannan tsarin ci gaba na shugaban kasa Roch Marc Christian Kabore shi ne na wuce kashi 6.2 cikin 100 na bunkasuwar shekara bisa matsakaici ta shekaru goman da suka gabata, zuwa a kalla kashi 8 cikin 100 a kowace shekara, a tsawon wa'adin mulkinsa na gaba, domin rage matsalar talauci da kashi 40 cikin 100 zuwa a kalla kashi 35 cikin 100 nan da shekarar 2020. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China