in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyya mai mulki a Burkina Faso ta lashe kujerun da dama a zaben kananan hukumomin kasar
2016-05-27 19:25:53 cri
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar Burkina Faso ta bayyana cewa, kwarya-kwaryar sakamakon zaben da ta fitar ya nuna cewa, jam'iyyar MPP mai mulkin kasar ce ta lashe galibin kujerun da aka yi takara kansu a zaben kananan hukumomin kasar da ya gudana ranar Lahadin da ta gabata.

Alkaluma na cewa, a daren ranar Laraba, jam'iyyar ta lashe kashi 58.91 cikin 100 na kujerun da aka fafata a kansu a mazabu 363, wato kwatankwacin kujeru 11,167.

Hukumomin wucin gadin kasar ce dai suka rusa majalisun kananan hukumomin da tun farko suke hannun jam'iyyar Compaore.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China