Jami'in ya ce ana zargin mutane 75 da hannu a lamarin, kuma yanzu haka ana tsare da mutane 50 daga cikinsu, yayin da aka ba da belin mutane 17 kana akwai mutane 8 da ba a tsare su ba.
A ranar 16 ga watan Satumban shekarar 2015 ne wasu sojoji da ke gadin fadar shugaban kasar da ya gabata suka kifar da gwamnatin wucin gadin kasar na dan wani lokaci, kafin daga bisani masu zanga-zanga da jami'an sojojin kasar su hambarar da su.
Bayan juyin mulki ne kuma aka kama sojoji da fararen hula da dama wadanda ke goyan bayan tsohon shugaba Blaise Compaore bisa zargin su da hannu a juyin mulkin.(Ibrahim)