in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
EU ta samar da wani tallafin jin kai ga kasashen Nijeriya, Nijar da Kamaru
2016-08-06 12:00:24 cri
Kwamitin kungiyar tarayyar Turai (EU) ya samar a ranar Alhamis da wani karin tallafin jin kai na kudin Euro miliyan 12.5 ga kasashen Najeriya, Nijar da Kamaru. A cewar kwamitin, miliyan 9 na Euro kimanin dalar Amurka miliyan 10 za su je ga Najeriya, Euro miliyan 2 ga Kamaru kana Euro miliyan 1.5 ga kasar Nijar.

Kwamitin tarayyar Turai ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa wannan sabon taimakon kudin ya zo bayan tashe tashen hankalin Boko Haram a arewacin Najeriya da suka janyo zaman dar dar sosai a shiyyar tafkin Chadi, tare da janyo gudun hijira na miliyoyin mutane.

Wannan karin taimakon kudade na EU zai mai da hankali kan taimakon gaggawa, musamman ma a fannonin abinci da abinci mai gina jiki, ruwan sha da kuma tsabta, da ma kiwon lafiya. Ya kamata a aiwatar da dukkan kokari domin tabbatar da ganin cewa shirye shiryen ayyukan jin kai sun isa ga wadanda dake cikin bukatar gaggawa, in ji kwamishinan tarayyar Turai mai kula da agajin jin kai da kula da bala'u, Christos Stylianides. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China