in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar Turai za ta kira taron musamman don tattauna batun ballewar Birtaniya daga EU
2016-06-25 12:33:32 cri
Shugaban majalisar kasashen Turai, Martin Schulz, ya bayyana a ranar Jumma'a cewa, za a kira taron musamman na majalisar kafin a kaddamar da taron kolin Tarayyar kasashen Turai EU a ranar 28 ga wata, inda za a zartas da kuduri kan yadda za a tantance sakamakon zaben raba gardama da aka yi a kasar Birtaniya, gami da matakan da za a dauka don tabbatar da ficewar kasar daga EU.

Kafin haka, mista Schulz ya jagoranci taron shugabannin jam'iyyun dake da kujerunsu a majalisar Turai, inda aka tattauna batun jefa kuri'ar raba gardama da aka yi a kasar Birtaniya don ganin ko za a balle kasar daga EU ko akasin haka. Daga bisani, Schulz ya gaya ma manema labaru cewa, za a zartas da kuduri a taron musamman da za a kira a birnin Brussels, daga baya za a mika kudurin ga taron shugabannin kungiyar EU dake tafe.

A cewar mista Schulz, yana bakin ciki matuka kan yadda jama'ar Birtaniya suka tsai da kudurin ballewar kasarsu daga EU, amma wannan niyya ce ta daukacin jama'ar kasar. Wannan lokaci ne mai wuya matuka ga kungiyar EU gami da kasar Birtaniya. Sai dai yanzu za a share fagen matakan za a za a dauka a nan gaba daga fannonin shari'a da na tsarin aikin.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China