in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
NATO da EU sun cimma hadaddiyar sanarwa game da karfafa hadin kai
2016-07-09 12:34:15 cri
An bude taron kolin kungiyar NATO a jiya Juma'a a birnin Warsaw, babban birnin kasar Poland. A yayin taron da za a shafe kwanaki biyu ana yinsa, za a mayar da hankali kan manyan batutuwa guda uku, ciki har da girka sojoji da kungiyar NATO ta yi a tsakiya da gabashin Turai, da hada kai tare da kasashe aminai a fannin tsaro, da kuma hada kai da kungiyar EU.

Kafin bude taron a wannan rana, babban sakataren NATO Jens Stoltenberg, da shugaban majalisar Turai Donald Tusk, da shugaban kwamitin EU Jean-Claude Juncker sun sa hannu kan hadaddiyar sanarwa, inda suka tsaida kudurin karfafa hadin kai tsakanin wadannan manyan kungiyoyi.

Sanarwar ta ce, NATO da EU suna kasancewa muhimman abokan hadin kai ga juna, yanzu suna bukatar karfafa hadin kansu don tabbatar da tsaro a Turai da kuma sauran yankuna, tare kuma da taimakawa kasashe makwabtaka da sauran abokai wajen tabbatar da zaman karko.

A lokacin hutu na taron kolin din kuma, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya yi ganawa da shugabannin EU Donald Tusk, da Jean-Claude Juncker, inda bangarorin biyu suka bayyana cewa, za su kara hadin kai don tinkarar kalubalen janyewar Burtaniya daga EU, da kuma sauran matsaloli. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China