in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar ANC tana kan gaba a zaben kananan hukumomin kasar Afirka ta kudu
2016-08-05 10:50:37 cri
Rahotanni daga kasar Afirka ta kudu na nuna cewa, jam'iyyar ANC mai mulkin kasar ce take kan gaba da yawan kuru'u a dukkan fadin kasar, a zaben kananan hukumomin kasar da ya gudana.

Sakamakon zaben na baya-bayan da aka fitar yana nuna cewa, jam'iyyar ANC ta samu kaso 54.15 cikin 100 na kuru'un da aka kada a fadin kasar, yayin da jam'iyyar Democratic Alliance (DA) take biye da ita da kaso 26.9 cikin 100.

Mai magana da yawun jam'iyyar Zizi Kodwa ya ce, wannan sakamakon ya sake nuna irin tabbacin da al'ummar kasar Afirka ta kudu suke da shi a kan jam'iyyar.

Masu sharhi kan al'amuran yau da kullum na ganin zabukan na wannan karo a matsayin mafi zafi tun bayan zaben shekarar 1994. Kuma wannan shi ne karon farko a cikin tarihin kasar, da jam'iyyun siyasa 200 da 'yan takara sama da 61,000 suke neman shugabancin majalisun kananan hukumomin kasar sama da 200. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China