in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban Afrika ta kudu ya bukaci musulmai su yaki masu haddasa rikicin addini
2016-07-07 09:36:14 cri
Mataimakin shugaban kasar Afrika ta kudu Cyril Ramaphosa ya bukaci al'ummar musulmai a fadin kasar da su hada karfi da karfe wajen tunkarar kalubalen dake damun duniya da suka hada da rikice-rikicen addini da nuna wariyar launin fata.

Ramaphosa, ya bayyana hakan ne a lokacin gudanar da bikin Sallar Idi ta wannan shekarar a Laudium, yammacin Pretoria, ya ce ya zama tilas a yi aiki tare da juna domin yakar laifuka da suka shafi ta da rikicin addini da wariyar launin fata da kuma aikata fyade.

Ramaphosa, ya ce ya zama wajibi al'ummar musulmi su hada kai wajen yin Allah wadai da yake-yake, da rikicin addini da ayyukan ta'addanci wadanda ke sanadiyyar hallaka rayukan al'umma, kuma su dage wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali domin ci gaban duniya baki daya.

Ya kara da cewar bayan kammala azumin watan mai tsarki, ya kamata a yi aiki tare wajen yakar talauci, da rashin daidaito, da rashin adalci, da yake-yake, da ayyukan ta'addanci wadanda ke sanadiyyar hallaka rayukan al'umma da ba su ji ba su gani ba.

Mataimakin shugaban kasar ya yabawa al'ummar musulmi dangane da rawar da suke takawa wajen sake ginawa kasa da kawo ci gaban kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China