in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci Afrika ta kudu ta dauki batun ta'addanci da muhimmanci
2016-06-09 13:21:17 cri
An bukaci gwamnatin Afrika ta kudu data dauki batun hare haren ta'addanci da muhimmanci kasancewar zai iya faruwa a ko ina a sassan duniya.

Wani fitaccen mai bincike a cibiyar nazarin al'amurran tsaro ta Afrika ta kudu Martin Ewi, ya fada a yayin zantawarsa da kamfanin dillancin labaraun kasar Sin Xinhua cewar, rashin fuskantar hare haren ta'addanci a kasar Afrika ta kudu ba yana nufin kasar ta tsira daga fuskantar duk wani harin ta'addanci ba.

Martin ya fadi hakan ne bayan da gwamnatin kasar ta nuna halin ko-in-kula da wani gargadin da ofisoshin jakadancin Amurka da Birtaniya dake Afrika ta kudun suka fitar game da barazanar yiwuwar kai hari a kasar.

A cewar gargadin, 'yan ta'adda suna kokarin kaddamar da harin ne a manyan kantunan zamani da kasuwanni, musamman ma a biranen Johannesburg da Cape Town a lokacin azumin watan Ramadan

To sai dai ministan tsaro na Afrika ta kudun David Mahlobo, ya fada a ranar Litinin cewar gwamnatin kasar ta lura da gargadin, amma bai kamata jama'a su tada hankalinsu ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China