Wata sanarwa da kakakin hedkwatar tsaron kasar Rabe Abubakar ya rabawa manema labarai, ta bayyana cewa, canjin shugabancin kungiyar ta Boko Haram ba zai yi wani tasiri ga matakan da sojojin kasar suke dauka da nufin kakkabe gyauro 'yan ta'addan a yankin arewa maso gabashin kasar ba.
A ranar Laraba ne dai kungiyar ta Boko Haram ta sanar da nadin Abu Musab Al-Barnawi a matsayin sabon shugaban kungiyar dake yammacin Afirka domin maye gurbin Abubakar Shekau. (Ibrahim)