in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron koli na G20 da za a yi a birnin Hangzhou zai zama taron G20 da zai fi yawan mahalarta kasashe masu tasowa
2016-08-04 11:29:53 cri
Ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a jiya Laraba cewa, taron koli na G20 na birnin Hangzhou zai zama taron da kasashe masu tasowa mafi yawa za su halarta a tarihin G20. A halin yanzu, ana gudanar da ayyukan share fage yadda ya kamata, muna da niyyar gudanar da wannan taro cikin nasara.

Bayan ganawarsa da takwaransa na kasar Laos Saleumxay Kommasith, ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi ya bayyana a gun taron manema labaru cewa, kasar Sin kasa ce mai tasowa mafi girma a duniya, kare ikon kasashe masu tasowa shi ne nauyin dake bisa wuyanta. Don haka, kasar Sin ta gayyaci kasar Laos, kasa mai rike da shugabancin kungiyar ASEAN da kasar Chadi, kasa mai rike da shugabacin kungiyar AU da kasashen Senegal da Kazakhstan da Masar da kuma sauran manyan kasashe masu tasowa don su halarci taron koli na G20 na Hangzhou. Ban da haka kuma, kasar Thailand, kasa mai rike da shugabancin kungiyar G77 tana fatan za ta iya halartar taron, kasar Sin tana tuntubarta a game da haka. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China