in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci kasashen Afirka da su magance matsalar kwararar likitocin nahiyar zuwa kasashen waje
2016-08-03 10:16:59 cri
An yi kira ga gwamnatocin kasashen Afirka da su dauki matakan da suka dace na ganin an dakile kaurar da likitocin nahiyar suke yi zuwa kasashen waje, matakin da masana suka ce yana sa kasashen nahiyar da ke yankin kudu da hamadar sahara hasarar tsabar kudaden da suka kai dala biliyan 2 wajen horas da likitocin.

Sakatare mai kula da harkar Ilimi a fadar shugaban kasar Kenya, Dr Fred Matiangi ya ce, likitocin nahiyar suna kaura zuwa kasashen yamma ne saboda karancin albashi da rashin kayayyakin bincike.

Matiangi ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar yayin bude taron hadin gwiwa na shekara-shekara na ma'aikatan lafiya (MEPI) karo na 6 da aka gudanar a birnin Nairobin kasar Kenya. Ya ce, kasashen Habasha, Kenya, Malawi, Najeriya, Afirka ta kudu,Tanzaniya,Uganda,Zambia da Zimbabwe sune suka fi hasarar kudade, sakamakon kaurar da likitocin kasashen suka yi zuwa kasashen waje. Yayin da a daya hannun kuma, kasashen Australia da Canada da Burtaniya da Amurka suka fi amfana wajen daukar irin wadannan likitoci da da ma can suke da kwarewa.

Taron na kwanaki uku ya hallara masu ruwa da tsaki a fannin ilimin likitanci daga ciki da wajen kasar, da wakilan makarantun horas da ma'aikatan lafiya daga kasashen Afirka, wakilan cibiyoyin da ke daukar nauyi da sauran abokan hulda wadanda ke horas da ma'aikatan kiwon lafiya da raya harkokin bincike a kasashen yammacin Afirka.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China