in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen kudancin Afrika zasu fuskanci na fuskantar rashin kyawun damina da suka jima basu ga irinta ba
2016-08-02 10:35:00 cri
Wani rahoto ya bayyana cewar, sakamakon matsalar fari ta El Niño, kasashen kudancin Afrika zasu fuskanci na fuskantar rashin kyawun damina da suka shafe shekaru basu ga irinta ba, lamarin ya haddasa magidanta na fama da mummunar matsalar karancin abinci.

Rahoton wanda hukumar gargadi game da karancin abinci wato FEW NET ta fitar, hasashen ya nuna cewar, adadin mutanen da suke fuskantar karanci abincin ya zarce kima, a kalla mutane miliyan 17 ne zasu fuskanci matsalar karancin abinci tsakanin watan Janairu zuwa Maris na shekarar 2017, wadanda suke matukar bukatar agajin gaggawa.

Rahoton ya ce, a karshen wannan daminar, magidanta da dama a kasashen Zimbabwe, da Malawi, da Mozambique, da Madagascar, da Lesotho, da Swaziland zasu yi matukar fuskantar karancin abinci.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China