in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Najeriya zata yi amfani da kwarewa wajen tunkarar tsagerun Niger Delta
2016-08-03 10:04:48 cri
Rundunar sojin Najeriya tace, jami'anta zasu yi amfani da kwarewa, da hanyoyi na lumana wajen tunkarar barazanar tsaro daga mayakan yankin Niger Delta mai arzikin mai.

Rear Admiral Joseph Okojie, shi ne kwamandan rundunar tsaron hadin gwiwa a yankin Niger Delta, ya shedawa manema labaru a birnin Yenagoa cewa, jami'an sojojin da aka tura a ranar Litinin zuwa yankin Kaima a jahar Bayelsa, na daya daga cikin matakan tabbatar da zaman lafiya a yankin.

An tura dakarun sojoji tare da kayayyakin aiki zuwa yankin na Kaima a jahar Bayelsa ne, sakamakon barazanar da tsagerun yankin Niger Delta ke yi na yunkurin karbe iko a yankin.

A watanni uku da suka shude, tsagerun yankin sun haifar da koma baya ga cigaban tattalin arzikin Najeriya, sakamakon kaddamar da hare hare, tare da lalata bututun danyen mai da iskar gas a yankin .(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China