Kaddamar da hari kan bututun man ya tilasta kamfanin na Agip dakatar da aikin hako danyen mai da kamfanin ke gudanarwa wanda a kowace rana yake hako gangar danyen man fetur kimanin dubu 65.
Tunda farko kungiyar tsagerun yankin Niger Delta Avengers, sun yi ikirari cikin wata sanarwa ta shafukansu na twitter cewar sun dauki alhakin kaddamar da hare haren.
Wannan hari dai na zuwa ne bayan sanarwar da gwamnatin kasar ta fitar na tsagaita bude wuta na tsawon makonni 2 domin tattaunawar sulhu da mayakan yankin mai arzikin mai da nufin lalubo bakin warware takaddamar cikin ruwan sanyi.