in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Najeriya na tura karin dakaru yankunan Niger Delta
2016-06-06 09:13:14 cri
Rundunar sojin Najeriya na tura karin dakarun ta yankunan Niger Delta mai arzikin mai, a wani mataki na dakile ayyukan tsagerun yankin.

Da yake tabbatar da hakan a birnin Yolan jihar Adamawa, babban hafsan sojojin saman kasar Air Mashal Sadik Abubakar, ya ce sojojin kasar ba za su yi kasa a gwiwa ba, wajen murkushe masu yiwa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa. Sadik ya kara da cewa sojojin ba za su dakata ba, har sai sun tabbatar da kare dukkanin yankunan kasar daga ayyukan bata gari.

Tun daga watan Fabarairun da ya gabata ne dai sabon gungun tsagerun yankin na Niger Delta da aka fi sani da 'Niger Delta Avengers", suka fara matsa kaimi wajen kaddamar da hare hare kan kayayyakin kamfanonin hakar danyen mai da iskar gas a wannan yanki. Sun kuma sha ikirarin lalata kayayyakin kamfanonin dake aikin hakar danyen man, suna masu ayyana bukatar neman 'yancin yankin na Niger Delta.

Rahotanni sun tabbatar da cewa hare haren da maharan ke kaddamarwa a baya bayan nan, sun jawo koma baya game da yawan danyen man da Najeriyar ke fitarwa zuwa ketare, ya zuwa ganga miliyan daya da dubu dari hudu a ko wace rana, adadin da ya yi kasa matuka da abun da kasar ke hakowa a baya.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China