Mayakan sun lalata rijiyar man ce sa'o'i 48 bayan da gwamnatin Najeriya ta bukaci 'yan tawayen na Avengers da su tsagaita bude wuta kana su koma teburin sulhu da mahukuntan kasar.
Sai dai tun farkon kungiyar ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa,ba za ta tattaunawa da wakilan gwamnatin ba.
Har yanzu dai babu wani karin bayani daga bangaren kamfanin na Chenvron ko hukumomin kasar ta Najeriya game da harin na baya-bayan nan.(Ibrahim)