in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya zata magance kalubalen yankin Niger Delta mai arzikin mai
2016-04-24 12:34:25 cri
Hukumomi a Najeriya sun tabbatar da cewar za'a kara samar da jami'an sojoji don fatattakar masu fasa bututun mai da yin garkuwa da mutane da kuma tsafe tsafe a yankin Niger Delta mai albarkartun mai.

Jami'in hukumar tsaron kasar Abayomi Olanisakin, shi ne ya tabbatar da hakan a Yenagoa, helkwatar mulkin jahar Bayelsa a loakacin da ya kai ziyarar aiki a rundunar hadin gwiwa ta sojojin kasar dake yankin Niger Delta.

Olanisakin yace, makasudun ziyarar tasa shine don cika umarnin da babban kwamandan tsaron Najeriya kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar na dakile ayyukan tsagerun yankin Niger Delta.

Yace a yayin ziyarar zai binciki halin da jami'an soji a yankin suke ciki game da irin kayayyakin aiki da suke bukata domin cigaba da ayyukansu don magance barazanar dake addabar yakin mai arzikin mai. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China