in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Brazil tana neman sauya tsohon dan wasansa da ya ji rauni
2016-08-02 16:27:11 cri
A ci gaba da share fagen gasar Olympics, kasar Brazil ta bukaci hukumar FIFA da ta ba ta izinin sanya karin sunan wani dan wasan kasar, cikin kungiyar wasan kwallon kafarta mai 'yan wasa 35, wadda za ta halarci wasannin Olympics na wannan karo tare da shi, don maye gurbin mai tsaron gida Fernando Prass, wanda ya ji rauni a hannunsa.

Hukuma mai kula da wasan kwallon kafa ta kasar Brazil, ta ce ya kamata a ba ta izinin maye gurbin Prass mai shekaru 38 a duniya, da wani tsohon dan wasan kasar na daban.

Bisa ka'idojin wasannin Olympics, ko wace kasa na da ikon sanya 'yan wasa 3 ne kacal wadanda shekarun su suka haura 22. Kuma cikin wannan tawaga ta Brazil banda shi Prass, sauran tsoffin 'yan wasan kasar 2 su ne Neymar da Renato Augusto.

Prass din wanda yake taka leda a kulob din Palmeiras na kasar Brazil, ya ji rauni ne a hannunsa na dama yayin da yake wasa, sa'an nan ya sake fama ciwon yayin wasan sada zumunta da aka buga tsakanin Brazil da Japan a ranar Asabar da ta wuce. Sakamakon binciken da aka yi masa, ya nuna cewa zai bukaci samun hutu har tsawon wasu makwanni, hakan ne kuma ya sanya Brazil din nuna bukatar maye gurbin sa da wani dan wasan mai shekaru sama da 22 na daban.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China