in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kudurin da IOC ta yanke game 'yan wasan Rasha ya haifar da mahawara a New Zealand
2016-07-27 20:14:22 cri

Kwamitin gudanar da harkokin wasannin Olympic na kasar New Zealand ko NZOC, ya yi amanna da kudurin da hukumar shirya wasannin Olympic ta kasa da kasa IOC ta yanke, na tantance 'yan wasan kasar Rasha tsaf, kafin kyale su su shiga gasar Olympic ta birnin Rio da za a bude, nan gaba cikin wata mai zuwa. Sai dai wannan ra'ayi ya sabawa na hukumar dake yaki da ta'ammalin da miyagun kwayoyi tsakanin 'yan wasa ta kasar wato DFSNZ. Inda wannan hukuma ke ganin mawuyaci ne IOCn ta iya tantance 'yan wasa yadda ya kamata kuma a kan lokaci.

Wannan batu dai ya haifar da zazzafar muhawara tsakanin sassan biyu, duba da a hannu daya, yadda (NZOC) ta fidda sanarwar amincewa da matakin na IOC, yayin da a daya hannun kuma DFSNZ wadda a baya ke goyon bayan dakatar da daukacin 'yan wasan Rashan daga shiga wannan gasa, ke ganin sabon matakin na IOC, tamkar tarnaki ne ga 'yan wasan Rashan, wadanda ke kiyaye dokar da ta jibanci mu'amala da miyagun kwayoyi.

Ita dai IOC ta dauki wannan mataki ne na yiwa 'yan wasan Rasha tantancewar kwaf, bayan da aka gabatar da rahoton "McLaren", wanda ya tabbatar da zargin da ake yi wa wasu daga hukumomin Rashan da hannu, wajen daukar nauyin 'yan wasa masu mu'amala da miyagun kwayoyi, ko kuma basu kariya.

Yanzu dai IOCn za ta bukaci 'yan wasan na Rasha, masu shirin shiga gasar birnin Rio da su gabatar da cikakkiyar shaidar nuna biyayya ga ka'idojin gasar, da kuma bada dama ta a yi musu gwaji a wajen kasar su.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China