in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya maraba da tattaunawar siyasa da bangarori daban daban na Burundi suka yi
2016-05-28 12:36:30 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ta yawun kakakinsa ne ya bayar da wata sanarwa a jiya Jumma'a, inda ya nuna maraba ga tattaunawar siyasa game da Burundi da aka yi a kwanan baya a birnin Arusha dake arewacin kasar Tanzania, ya kuma jaddada cewa, yin shawarwari dake kunshe da bangarori daban daban ita ce hanya daya tak da za ta iya warware rikicin siyasa da Burundi take fuskanta.

Sanarwar ta ce, an gudanar da tattaunawar siyasa kan rikicin Burundi a ranar 21 zuwa 24 ga wata, mai shiga tsakani na kungiyar EAC, kuma tsohon shugaban kasar Tanzania Benjamin Mkapa ne ya shugabanci tattaunawar. Mkapa ya ce, za a kira bangarorin Burundi da ba su halarci tattaunawar ba don su shiga tattaunawa ta sabon zagaye, game da haka kuma Ban Ki-Moon ya nuna yabo sosai kan matakin.

Baya ga haka, Ban Ki-Moon a cikin sanarwar ya jaddada cewa, idan ana son warware rikicin siyasar Burundi, dole ne a gudanar da tattaunawa bisa tushen kundin tsarin mulkin Burundi, kuma bisa yarjejeniyar shimfida zaman lafiya da zaman jituwa na Burundin. Ban Ki-Moon ya bayyana goyon baya ga kokarin da ake yi wajen warware rikicin Burundi ta hanyar lumana, ya kuma bayyana cewa, MDD na fatan taka rawa a kai.

Tun daga watan Aflilun shekarar 2015, sakamakon rashin jin dadi da jama'ar kasar suka nuna ma jam'iyya mai rike da ragamar mulki wadda ta nuna goyon baya ga shugaba Pierre Nkurunziza da ya yi tazarce kan shugabanci, kasar Burundi ta fada cikin tashen tashen hankali da zanga-zanga. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China