in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Burundi ya gana da tawagar sada zumunta ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin
2016-06-01 11:15:15 cri
A ranar 31 ga watan Mayu, shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza ya gana da tawagar sada zumunta ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da ke karkashin jagorancin Duan Yuying, wato mataimakin sakataren kula da harkokin hukumomin da ke karkashin jagorancin kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin.

Nkurunziza ya ce, kasarsa ta jinjinawa goyon baya da Sin ta nuna mata don warware rikicin da ya barke sakamakon babban zaben kasar, jam'iyyar FDD ta kasar Burundi tana fatan yin koyi da nasarorin da Sin ta samu wajen tafiyar da harkokin kasa, da kyautata kwarewar mulki.

A nasa bangare kuma, Duan ya ce, jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin tana fatan karfafa mu'amala da jam'iyyar FDD ta Burundi, don kyautata dangantakar kasashen biyu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China