Masu bada taimako na kasa da kasa 6 sun mutu a kasar Somaliya a farkon watanni 6 na bana
Bisa rahoton da ofishin daidaita harkokin jin kai na MDD ya gabatar a ranar 29 ga wata, an ce, masu bada taimako na kasa da kasa 6 sun mutu a kasar Somaliya a farkon watanni 6 na bana, yayin da mutane 8 suka ji rauni, kana aka yi garkuwa da wasu masu bada taimako a lokacin.
Rahoton ya yi nuni da cewa, a farkon watanni 6 na bana, an fuskanci hare-hare 80 da aka kaiwa hukumomin jin kai dake kasar Somaliya, wanda ya zarce na makamancin lokacin shekarar 2015. (Zainab)