in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu boma-bomai sun fashe a dab da filin jiragen sama na Mogadisu
2016-07-26 19:39:08 cri
Wani jami'in tsaron kasar Somaliya ya tabbatar a yau Talata cewa, an samu fashewar wasu boma-bomai har sau biyu a dab da filin jiragen saman birnin Mogadishu,fadar mulkin kasar Somaliya, wadanda suka haddasa mutuwar mutane a kalla 8 yayin da mutane da dama suka ji rauni.

Bam na farko ya fashe ne a kofar shiga filin jiragen saman, kana bam na biyu kuma ya fashe a kofar shiga sansanin tawagar musamman ta kungiyar AU dake kasar Somaliya dake dab da filin jiragen saman.

Kakakin tawagar musamman ta AU dake kasar Somaliya ya bayyana cewa, an kai harin kan sansanin dake dab da filin jiragen saman, kana yana kusa da sansanin MDD da wasu ofisoshin jakadancin kasashen yammacin duniya dake kasar Somaliya. Har yanzu ba a tabbatar da asalin kasashen mutanen da suka mutu a sakamakon fashewar boma-boman ba.

Kungiyar Al-Shabaab ta kasar Somaliya ta sanar da alhakin kai wannan hari. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China