MDD da AU sun yi Allah wadai da hare-haren bama-bamam da aka kai a kusa da filin jiragen sama na Mogadishu
Wakilan MDD da kungiyar tarayyar Afirka ta AU da ke kasar Somaliya, sun yi Allah wadai da tagwayen hare-haren bama-bamai na kunar bakin wake da aka kai a harabar filin jiragen sama na kasa da kasa da ke Mogadishu,babban birnin kasar Somaliya, wadanda suka haddasa mutuwar mutane a kalla 13 kana wasu mutane biyar kuma suka jikkata.(Ibrahim)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku