in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An hallaka mayakan Al-Shabaab 7 a kudancin Somaliya
2016-06-19 13:42:46 cri
A kalla mayakan Al-Shabaab 7 ne aka hallaka sannan aka cafke wasu 5 na dakarun kunigyar a yayin wani bata kashi da aka gwabza tsakanin dakarun sojin Somaliya dake samun goyon bayan dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika da yammacin ranar Jumma'a a kudancin Somaliya.

Wani jami'in sojin Somaliya Ali Digaal shi ne ya tabbatar da hakan, a cewarsa an yi dauki ba dadin ne a a wani yanki kusa da garin Barowe dake shiyyar Shabelle.

Digaal ya shedawa 'yan jaridu cewar, fadan ya barke ne a lokacin da mayakan na Al-Shabaab suka yi yunkurin bude wuta kan tawagar mayakan wanzar da zaman lafiyar a kan hanyarsu ta zuwa garin Barowe.

To sai dai kungiyar ta Al-shabaab ta yi ikirarin cewa ita ce ta yi nasara, har ma ta ambata cewar ta kone 3 daga cikin tankokin yakin dakarun na AMISCOM.

Dakarun wanzar da zaman lafiyar dai, na ci gaba da farautar mayakan na Al-Shabaab a yankuna da dama na kudancin birnin Mogadishu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China