in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Nijer sun mamaye sansanonin kungiyar Boko Haram guda biyu
2016-07-30 12:48:29 cri
A jiya Jumma'a 29 ga wata, hukumar hafsan hafsoshin rundunar sojan Nijer ta ba da sanarwar cewa, a safiyar ranar Alhamis 28 ga wata, sojojin Nijer sun kwace wani kauye na jihar Diffa dake kudu maso gabashin kasar Nijer, da garin Damasak na Nigeriya daga hannun kungiyar Boko Haram.

Bisa sanarwar, a yayin da suke musayar wuta da 'yan kungiyar Boko Haram, sojojin Nijer sun sami taimako daga sojojin sama na hadaddiyar rundunar JTF, tare da samun babbar nasara.

A ranar 25 ga wata, gwamnatin Nijer ta tura tankuna da manyan motocin yaki sama da 10 zuwa yankin iyakar kasa tsakanin Nijer da Nijeriya domin dakile dakarun kungiyar Boko Haram, inda makasudin aikin shi ne kawar da sansanonin kungiyar dake yankin kogin Komadugu Yobe, domin kwace garin Damasak tun da wuri, garin da ake tsammanin cewa, wata muhimmiyar makarfafa ce ta kungiyar.

Bisa sanarwar da hadaddiyar rundunar JTF ta bayar, an ce, a sa'i daya sojojin Nijeriya su ma sun fara aikin yaki da kungiyar Boko Haram, domin hadin gwiwa da sojojin Nijer.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China