in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe taron tattaunawa kan hadin gwiwar kafofin watsa labaru a tsakanin Sin da Afirka karo na 3
2016-06-22 14:00:05 cri
A jiya ne aka rufe taron tattaunawa kan hadin gwiwar kafofin watsa labaru a tsakanin Sin da Afirka karo na 3 a nan birnin Beijing, inda bangarorin biyu suka daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa 15, daga bisani kuma suka bayar da sanarwar bayan taro, wanda ya nuna alkiblar raya hadin gwiwar kafofin watsa labaru a tsakanin Sin da Afirka a nan gaba.

Mataimakin shugaban hukumar kula da harkokin watsa labarai da dab'i da rediyo, telebijin da fina-finai ta majalisar gudanarwar kasar Sin Tong Gang ya bayyana a gun bikin rufe taron cewa, an shirya taron ne yayin da aka cika shekaru 60 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Sin da kasashen Afirka, yawan mahalarta taron ya zarce yawan wadanda suka halarci tarukan da aka gudanar a baya, kana an samu babban sakamako a gun taron.

Rahotanni na cewa, yarjejeniyoyi 15 da sassa biyu suka sanyawa hannu sun hada da takardar fahimtar juna ta hadin gwiwar hukumar kula da harkokin watsa labaru da dab'i da rediyo da telebijin da fina-finai ta kasar Sin da hukumar watsa labaru ta kasar Zimbabwe, iznin watsa shirye-shirye 4 a kasashen Mauritania, Uganda, Nijer da Togo da dai sauransu.

A cikin sanarwar hadin gwiwar, kasashen Afirka sun kuma nuna goyon baya ga Sin da kasashen da rikicin tekun kudancin Sin ya shafa da su warware matsalar ta hanyar yin shawarwari cikin lumana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China