in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta yi kira ga kasar Amurka da ta kawar da kungiyar ta'addanci daga kungiyar masu adawa mai sassaucin ra'ayi ta kasar Syria
2016-05-28 13:28:42 cri
Shugaban hukumar bada umurni ta kasar Rasha Sergei Rutskoy ya bayyana a ranar 27 ga wata cewa, kungiyar ta'addanci ta Al-Nusra ta yi amfani da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta kasar Syria, don zama tare da kungiyar dake adawa da gwamnati mai sassaucin ra'ayi ta kasar, hakan dai ta magance harin da sojojin Rasha suka kaiwa musu. Kasar Rasha ta yi kira ga kasar Amurka da ta bi yarjejeniyar, don kawar da kungiyar ta'addanci daga kungiyar mai adawa na sassaucin ra'ayi.

Rutskoy ya bayyana a gun taron manema labaru da ma'aikatar tsaron kasar ta gudanar a wannan rana cewa, an kyautata halin tsaro da ake ciki a kasar Syria, an kwantar da hankali a wuraren da aka dakatar da ayyukan soja. Amma kungiyar Al-Nusra tana yunkurin lalata yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da tsananta halin da ake ciki a wasu yankunan kasar Syria. Kana kuma kungiyar Al-Nusra ta yi amfani da yarjejeniyar don zama tare da kungiyar da ke adawa da gwamnati mai sassaucin ra'ayi ta kasar don magance harin sama da Rasha take kai mata.

Rutskoy ya kara da cewa, a halin yanzu, kungiyar ta'addanci ta samu isassun makamai, kuma ta mayar da karfin sojansu, kana sun fara kai hare-hare a birnin Aleppo da yankin Homs. A kwanakin baya, Rasha ta bada shawara ga kasar Amurka da su hada kai don kai hare-haren sama ga kungiyar mai tsattauran ra'ayi da ta ta'addanci a kasar Syria, amma Amurka ba ta amsa shawarar Rasha ba. A cewar Rutskoy, wannan zai haddasa tsanantar da halin da ake ciki a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China